in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka da Turkiya sun yi alkawarin yin kokarin kawar da barazanar kungiyar IS ta hanyar siyasa
2016-01-24 13:30:36 cri
A jiya Asabar 23 ga wata, mataimakin shugaban kasar Amurka, Joseph Biden dake ziyara a birnin Istanbul na Turkiya, ya bayyana cewa, Amurka da Turkiya sun yi alkawarin karfafa hadin gwiwa tsakaninsu, a kokarin gano wata hanyar siyasa ta kawar da barazanar da kungiyar IS mai tsattsauran ra'ayi ke yima Syria.

A wannan rana, a gun taron manema labaru, Joseph Biden ya bayyana cewa, sun san cewa zabi mafi kyau ne a kawar da barazanar kungiyar IS ta hanyar siyasa, amma kuma ba za a yi alkawarin rashin daukar matakan soja ba.

Ban da haka, Joseph Biden ya kara da cewa, kasashen biyu sun amince da karfafa hadin gwiwa a fannonin samun sakwannin asiri, da nuna goyon baya ga sojojin wurin da sauransu, domin yaki da kungiyar IS.

Kasar Turkiya ta yi iyaka da Syria da Iraki, shi ya sa ta masu tsattsauran ra'ayi su kan bi ta kasar domin shiga kungiyar IS. Sakamakon karuwar matsin lamba daga kasa da kasa, da abkuwar harin ta'addanci na kunar bakin wake da kungiyar IS ta yi, wanda a bara ya kai ga haddasa mutuwar mutane sama da 130 a birnin Ankara, hedkwatar kasar Turkiya, da yankin Sanliurfa dake kudu maso gabashin kasar, gwamnatin Turkiya ta kara karfin yaki da kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi a kasar da dakaru masu tsattsauran ra'ayi dake ratsa kasar.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China