in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi tur da kaddamar da hari kan sansaninta dake Mali
2016-02-13 12:35:11 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon, ya yi Allah wadai game da harin ta'addanci da aka kaddamar kan ofishinta dake kasar Mali MINUSMA, lamarin da ya yi sanadiyyar hallaka jami'an dake aikin wanzar da zaman lafiya 5 da kuma jikkata a kalla mutane 30.

An kaddamar da harin ne kan ofishin na MINUSMA wanda ke garin Kidal a arewacin Mali a ranar Jumma'ar da ta gabata.

A sanarwar da mai magana da yawun magatakardan MDD ya fitar, ya bayyana kaddamar da hare hare kan jami'an aikin wanzar da zaman lafiya a matsayin yin keta dokokin kasa da kasa da suka haramta aikata laifukan yaki, sannan ya bukaci gwamnatin Mali da ta gaggauta gudanar da bincike domin zakulo wadanda ke da hannu a kai harin domin hukunta su.

Ban, ya kara da cewa kaddamar da hari kan ofishin na MINUSMA, ba zai taba sanyaya gwiwa MDD ba a yunkurinta na tallafawa gwamnatin kasar Mali domin samun dawwaumamman zaman lafiya da tsaron rayukan al'ummar kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China