in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci matakan gaggawa domin yaki da rashin hukunci a Afrika ta Tsakiya
2016-02-11 13:13:52 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake jamhuriyar Afrika ta Tsakiya (MINUSCA) ta bukaci a ranar Laraba ganin an dauki matakan gaggawa domin yaki da rashin hukunci da suka shafi ayyukan tauye 'yancin dan Adam da aka aikata a cikin watan Satumba da Oktoban shekarar 2015 a cikin wannan kasa.

A cikin wani rahoton da za a fitar ba da jimawa ba, masu bincike na MINUSCA sun tattara bayanai masu muni sosai kan ayyukan cin zarafin dan Adam da aka gudanar daga ranar 26 ga watan Satumba zuwa 20 ga watan Oktoban shekarar 2015 a Afrika ta Tsakiya, in ji wata sanarwar MINUSCA.

Haka kuma, sun gano lalata da karbe kaddarori, har ma da cinna wuta a gidaje da dama tare da sace kayayyakin wasu kungiyoyin gwamnati da na kungiyoyi masu zaman kansu, a cewar wannan sanarwa.

Shugaban tawagar MINUSCA, Parfait Onanga-Anyanga, ya bayyana damuwarsa game da iyuwar ko masu hannu kan wadannan ayyukan keta hakkin dan Adam ko za su amfana da rashin hukunta su, da kuma yin kira ga hukumomin Afrika ta Tsakiya da su dauki matakan gaggawa yadda ya kamata domin gurfanar da masu hannu kan wadannan munanan ayyuka gaba kotu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China