in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya bukaci a kaddamar da yaki kan kungiyoyin 'yan ta'adda ta yanar gizo
2016-02-13 12:09:48 cri
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Mista Liu Jieyi ya bukaci a kara kaimi don yakar kungiyoyi 'yan ta'adda dake cin karensu babu babbaka ta hanyar amfani da shafukan yanar gizo da na sada zumunta.

Mista Liu Jieyi, ya furta hakan ne a lokacin babban taron MDD, ya bayyana cewar kungiyoyin 'yan ta'adda na yin amfani da shafukan yanar gizo wajen isar da sakonninsu na muryoyi, da yada akidunsu na tsattsaurin ra'ayi, da daukar ma'aikata da tattara kudaden da suke amfani da su da kuma gudanar da ayyukan ta'addaci, don haka Liu ya nuna bukatar daukar matakai domin dakile aniyar kungiyoyin 'yan ta'adda.

Wakilin na kasar Sin na dindindin a MDD, ya bukaci kasashen duniya da hukumomin MDD masu ruwa da tsaki, da su dauki tsauraran matakai game da dokokin da suka shafi amfani da shafukan yanar gizo domin dakile aniyar 'yan ta'adda.

Sannan ya bukaci bangarorin da abin ya shafa, da su yi aiki kafa da kafa wajen yakar ayyukan ta'addanci.

Liu ya ce, sam bai kamata mu danganta wata kabila ko addini da ayyukan ta'addanci ba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China