in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon kasar Sin ya bayyana muhimmancin shiga tsakani wajen warware riginginmu
2016-02-12 12:59:49 cri
Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Li Jieyi, ya bayyana muhimmancin daukar matakan kandagarki, da na shiga tsakani wajen warware riginginmun dake addabar sassa daban daban na duniya.

Mr. Liu ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis, yayin zaman kwamitin tsaron MDD, yana mai cewa hanyoyin diflomasiyya su ne mafiya dacewa maimakon barazana ko sanya takunkumi.

Kaza lika manzon na Sin ya bayyana cewa, ya dace a rika sauraron ra'ayoyin sassan da ke fuskantar tashe tashen hankula, wanda hakan ne kadai zai baiwa kwamitin tsaron damar daukar matakai mafiya dacewa. Har wa yau ya yi kira ga kwamitin tsaron da ya maida hankali ga magance manyan dalilan dake haifar da barazana ga tsaro da zaman lafiyar duniya, kamar yadda hakan ke kunshe cikin dokokin MDD.

Daga nan sai ya jaddada bukatar tuntubar mambobin kwamitin tsaron kan dukkanin manufofi, da matakan da ake nazarta, domin samun cikakken hadin kai a ayyukan kwamitin. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China