in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu ya yi Allah wadai da harin ta'addaci da aka kaddamar kan ofishinta a Mali
2016-02-13 12:15:25 cri
Kwamitin tsaro na MDD yayi kakkausar suka game da harin ta'addanci da aka kaddamar kan ofishinta dake kasar Mali.

A sanarwar da kwamitin ya fitar, ya bukaci gwamnatin Mali da ta gaggauta gudanar da bincike domin zakulo wadanda ke da hannu a kai harin domin hukunta su.

Kwamitin mai mutane 15 ya bayyana kaddamar da hare hare kan jami'an aikin wanzar da zaman lafiya a matsayin yin karan tsaye ga dokokin haramta laifukan yaki na kasa da kasa.

Sanarwar ta bayyana dukkan nau'in hare haren ta'addanci a matsayin manyan abubuwan dake yin baraza ga zaman lafiyar duniya.

A yanzu a kara tsaurara tsaro a yankin tun bayan kaddamar da wadannan hare hare. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China