in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Zimbabwe tana neman taimakon abinci
2016-02-10 17:53:56 cri
Gwamnatin kasar Zimbabwe ta yi kira da a agazama mata da kudade sama da dala biliyan 1.5 domin ta sayo kayan abinci kana ta gyara kayayyakin noman raninta da suka lalace.

Mataimakin shugaban kasar Emmerson Mnangagwa wanda ya bayyana hakan a birnin Harare, fadar mulkin kasar yayin bikin kaddamar da gidauniyar neman taimako, ya ce gwamnati na shirin shigo da tan miliyan 1.4 na hatsi a wannan shekara, domin rabawa 'yan kasar kimanin miliyan 3 da matsalar fari ta shafa.

Kasar Zimbabwe wadda ta dogara da harkar noma wajen samun kudaden shiga, yanzu haka tana fama da matsalar farin da ba ta taba ganin irinsa ba yau kusan shekaru 60 da suka gabata sakamakon matsalar sauyin yanayi ta El Nino. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China