in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar shugaba Xi Jinping a Zimbabwe za ta amfanawa jama'ar kasashen biyu
2015-11-27 10:27:51 cri

A farkon watan Disamba ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai kai ziyara a kasar Zimbabwe dake kudancin nahiyar Afirka. A jiya Alhamis jakadan Sin dake kasar Zimbabwe Huang Ping ya bayyanawa 'yan jaridan kafofin watsa labaru na Sin cewa, ziyarar shugaba Xi Jinping za ta sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Zimbabwe a dukkan fannoni, kuma nasarorin da za a samu za su amfanawa jama'ar kasashen biyu.

Huang Ping ya yi nuni da cewa, kasashen Sin da Zimbabwe sun taimaka da juna yayin da suke raya tattalin arziki da zamantakewar al'ummarsu, kana an samu nasarori kan hadin gwiwar da ke tsakaninsu. Kasar Sin tana daukar kasar Zimbabwe a matsayin abokiyar cinikayya ta biyu kana kasa ta farko a bangaren zuba jari, kuma hukumomin hada-hadar kudi na kasar Sin sun tattara kudi tare da zuba jari ga kamfanonin Sin don su gudanar da manyan ayyukan fadada ayyukan more rayuwa a kasar Zimbabwe kamar filin jiragen sama na Victoria Falls da tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa da ke kudancin gabar tebkin Kariba da dai sauransu. A yayin ziyarar shugaba Xi Jinping a kasar Zimbabwe, kasashen biyu za su daddale wasu yarjejeniyoyin hadin gwiwa kan ayyukan more rayuwa. Bayan kammala wadannan manyan ayyuka, ana fatan za a kawo karshen matsalolin rashin wutar lantarki, da sufuri da dai sauransu, kuma hakan zai taimaka wajen raya tattalin arzikin kasar ta Zimbabwe. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China