Ghana za ta karbi bakuncin dandalin Afrika kan kiwon lafiya da 'yanci ta fuskar jama'i
2016-02-09 12:47:43
cri
Kasar Ghana za ta karbi daga ranar Laraba zuwa Jumma'a matan shugabannin kasashen Afrika da za su halarci wani dandali kan kiwon lafiya da 'yanci ta fuskar jama'i. Wannan dandali na cikin wani shirin na tsawon lokaci da ke da manufar gina da kuma samar da wata tattaunawar shiyya kan kiwon lafiyar jama'i da haihuwa da 'yanci a wannan fanni, a cewar wata sanarwa ta cibiyar matar shugaban kasar Ghana a ranar Litinin. Kimanin mahalarta 500 da ke wakiltar bangarorin daban daban na masu ruwa da tsaki da kungiyoyin yankunan nahiyar Afrika da za su halarci wannan dandali. (Maman Ada)