in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: Sin ba za ta janye daga manyan batutuwan da kasa da kasa ba
2016-02-05 10:48:57 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyanawa 'yan jarida bayan da ya halarci taron samar da gudummawar jin kai ga kasar Syria karo na 4 a jiya Alhamis cewa, a wannan karo, ya canja jadawalin ziyararsa yayin da yake ziyara a kasashen Afirka don ya halarci taron samar da gudummawar jin kai ga kasar Syria a kasar Birtaniya, wannan yana nufin cewa, Sin ba za ta kau da kai daga manyan batutuwan da kasa da kasa suke sa mayar da hankali a kansu ba.

Wang Yi ya jaddada cewa, Sin ta yi kira ga gwamnatin kasar Syria da kungiyoyin 'yan adawar kasar da su ba da muhimmanci ga moriyar jama'ar kasar Syria. Ya ce, kamata ya yi su halarci shawarwarin zaman lafiyar kasar ba tare da gindaya wani sharadi ba, da sa kaimi ga yin shawarwarin shimfida zaman lafiya sannu a hankali, ciki har da batutuwan amincewa da shigar da kayayyakin jin kai a kasar, da tsagaita bude wuta da dai saurausu, ta haka ne za a imance da juna sannu a hankali.

Wang Yi ya kara da cewa, a kwanakin baya, bi da bi ya gana da wakilan gwamnatin kasar Syria da na kungiyoyin 'yan adawa a birnin Beijing, inda ya yi kokarin shawo kansu da su halarci taron shawarwarin shimfida zaman lafiya na kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China