in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi maraba da taron Geneva karo na biyu a kan batun Syria
2013-11-26 19:49:01 cri
A ranar Talatan nan 26 ga wata, kasar Sin ta yi maraba tare da nuna goyon bayanta ga taro na biyu a Geneva game da batun kasar Syria, tana mai kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa da su matsa kaimi wajen tsara wani shiri a siyasance domin fitar da sakamako mai karko.

Babban magatakarda na MDD Ban Ki-Moon ya sanar da cewar, za'a yi taron Geneva karo na biyu a ranar 22 ga watan Janairun shekara mai zuwa.

A game da lamarin, kasar Sin ta bakin kakanin ma'aikatar harkokin wajen kasar Qin Gang ta ce, wannan ci-gaba yana da muhimmanci wajen aiwatar da kudiri mai lamba 2118 na kwamitin tsaron MDD., sannan zai ingiza warware matsalar a siyasance, wanda shi ne abin da kasar Sin ta dade tana kiran a bi.

Haka kuma Sin ta yi kira ga dukkannin bangarorin da al'amarin Syria ya shafa da su mai da muhimmanci a kan muradun kasa da na al'ummar kasar, su shiga tattaunawar siyasa, su kuma yi aiki da sauran kasashen duniya wajen shirya babban taron.

A fadar Qin Gang, kasar Sin za ta ba da nata gudummuwa a game da wannan taro.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China