in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya yi kiran karin tallafin Turai wajen yaki da ta'addanci
2016-02-04 09:53:58 cri
Shugaban tarayyar Najeriya, Muhammadu Buhari, ya yi jawabi a ranar Laraba a gaban majalisar tarayyar Turai, da ke zaman taronta a Strasbourg na kasar Faransa, inda yayi kira ga kungiyar tarayyar Turai da ta kara taimakonta ta fuskar yaki da ta'addanci.

Shugaban majalisar tarayyar Turai Martin Schulz ya tarbi Muhammadu Buhari, da ya zama shugaban Najeriya a cikin watan Mayun shekarar 2015, tare da nuna yabo kan muhimman sauye sauyen da ya bullo da su musammun ma ta fuskar yaki da ta'addanci gaban yawaitar ayyukan ta'addanci na kungiyar Boko Haram.

A cikin jawabinsa, mista Buhari ya nuna godiya ga yawan kasashen tarayyar EU da suka bada kokari wajen ganin an ceto 'yan matan garin Chibok da aka sace a cikin watan Afrilun shekarar 2014, a arewa maso gabashin Najeriya, lamarin da ya janyo allawadai a duniya baki daya.

Ta fuskar yaki da ta'addanci, "muna iyakacin kokari" in ji shugaban Najeriya a gaban 'yan majalisun tarayyar Turai. "An karya lagon kungiyar Boko Haram sosai na kai manyan hare hare a sassan kasa" in ji shugaba Buhari. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China