in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi allawadai da hare haren ta'addanci na Boko Haram a Najeriya
2016-02-03 10:28:46 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya yi tir da allawadai da babbar murya a ranar Talata da hare haren ta'addanci na ranar 30 ga watan Janairu da kungiyar Boko Haram ta kai kauyen Dalori, wanda ya yi kusa da birnin Maiduguri da ke arewa maso gabashin Najeriya.

A kalla mutane 85 suka mutu a wannan hari. Maharan sun rika harbi kan mazauna wurin kafin kuma su afkawa kauyen wuta.

A cikin wata sanarwa, mambobin kwamitin sulhu sun isar da ta'aziyarsu ga iyalai da abokan wadanda lamarin ya rutsa dasu, tare da jaje ga al'umma da gwamnatin Najeriya.

Kwamitin ya nuna yabo da kokarin wannan shiyya, musammun game da kafa rundunar hadin gwiwa domin yaki da kungiyar Boko Harma yadda ya kamata, tare kuma da bada kwarin gwiwa wajen kara samun nasarori a wannan fanni. Mambobin kwamitin sun jaddada wajabcin ganin an gurfanar da masu hannu game da wadannan hare hare gaban kotu.

Birnin Maiduguri, na kunshe da yawan mutane kimanin miliyan 2.6, kuma miliyan 1.6 sun kasance 'yan gudun hijira a cewar MDD, birnin da ya sha fama da hare haren ta'addanci sau da yawa a wadannan watanni na baya baya nan.

Kungiyar Boko Haram ta bullo a birnin na Maiduguri a shekarar 2002, kafin a shekarar 2009 ta zafafa hare harenta da suka kashe mutane fiye da dubu 17 a Najeriya da kuma tilastawa wasu mutane miliyan 2.6 barin muhalinsu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China