in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta kwato sama da dala triliyon 2 daga cikin wadanda aka sace
2016-02-04 09:45:21 cri
Najeriya ta ce ta samu kwato sama da dala triliyon 2 daga cikin wadanda wassu jami'an gwamnati da kungiyoyin 'yan damfara suka yi watandar su a baitulmalin kasar cikin shekaru 12.

Kamar yadda Ministan shari'ar kasar Abubakar Malami yayi bayani cikin wata sanarwa da ya fitar yace kudaden hukumar yaki da laifukan da suka shafi kudaden kasar wato EFCC ce ta kwato su.

Malami yace matsayin da laifuffukan da suka shafi kudade ya kai koli a muni saboda ba kawai bangaren kudi da ya samu matsala ba saboda yadda aka wargaza tsarin shi har ma da bangaren shari'a saboda rashin sahihanin tsarin da za'a bi a shari'a , raunin hukumomin tsaro da rashin kayan aiki a bangaren shari'an daga sauran bangarori daban daban.

A watan jiya, Gwamnatin Najeriyar ta ce ana shirin yin shari'a wassu manyan jami'an gwamnati a kalla su 55 da aka same su da laifin wawushe kudin kasa lokacin da suke aiki karkashin gwamnatocin da suka shude.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China