Babban taron kungiyar tarayyar Afrika (AU) a birnin Addis-Abeba na kasar Habasha ya yanke shawara cewa dandali kan tsaron teku da cigaba a Afrika zai gudana a ranar 15 ga watan Oktoba mai zuwa a birnin Lome. Haka kuma, kungiyar ta AU na fatan ganin wannan dandali ya kai ga cimma wani kundin aiki na Afrika dake nasaba da tsaron nahiyar da kuma tsaron teku. AU ta kuma amince da sharawar gwamnatin Togo na karbar wani taron kwamitin kwararru domin shirya taron na Lome. (Maman Ada)