Gnassingbe ya hau karagar mulkin kasar ne a shekara ta 2005 bayan wani zaben gaggawa sakamakon mutuwar mahaifin sa kuma tsohon shugaban kasar Janar Eyadema Gnassingbe wanda ya yi mulkin kasar na tsawon shekaru 38 wato daga shekara ta 1967 zuwa 2005.
An sake zaben Faure Gnassingbe a karo na biyu a watan Maris na shekara ta 2010 da kashi 60.89 a cikin 100 da kafatanin kuri'un da aka kada inda ya doke abokin hamayyar sa Fabre mai kashi 33.94.( Fatimah)