in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An jinjina ma kamfanin kasar Sin a Togo saboda kafa fitilu masu aiki da hasken rana
2015-08-22 13:30:06 cri
Mahukunta a kasar Togo sun bayyana jin dadin su da matsayin da kamfanin kasar Sin ZTE ta kai na aiwatar da kammala hada fitilun kan titituna masu aiki da hasken rana kashi na farko guda 13,000.

Kamar yadda wata majiya ta tabbatar ma kamfanin dillanci labarai na Xinhua, makasudin wannan aikin shi ne rage kudin da kasar ke kashewa a lantarki. Yanzu haka akwai fitilun kan tituna guda 7,042 da aka rigaya aka kafa a manyan titunan kasar ta Togpo a kashin farko. Ana sa ran kashi na biyun zai fara a watan Satumba mai kamawa wanda za'a kafa fitilu 5,958.

A cewar Abiyou Tcharabalo, daraktan makamashi a ma'aikatar makamashi da ma'adinai, aikin na daga cikin tsarin da kasar ta Togo ta dauka domin inganta sabon shirin yin amfani da makamashi kuma an tsara shi ne ma kasashen duniya da zummar rage kudin lantarki da ake biya a unguwanni.

Aikin samar da lantarkin tituna a kasar Togo shi ne mafi girma kuma wanda aka biya kudi sosai a kan shi, idan aka kwatanta da sauran ayyukan da kamfani ZTE a kasashen Benin, Burkina faso, Niger, Nigeriya, Djibouti da kuma Senegal.

Kamfanin ZTE dai ita ce a kan gaba a bangaren samar da kayayyakin sadarwa a kasar Sin. Yanzu haka tana da shekaru 15 na kwarewar aiki a wannan bangaren. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China