Gwamnatin Togo ta gabatar da sakamakon bincike na INSSED dake bayyana kyautata zaman rayuwar al'umma
Gwamnatin kasar Togo ta fitar a ranar Talata da sakamakon wani bincike da hukumar kididdiga ta kasa da nazarin tattalin arziki da al'umma (INSSED) ta gudanar dake nuna kyautatuwar yanayin zaman rayuwar al'ummar kasar Togo. Hanyoyi da dama na kyautatuwar zaman rayuwar al'umma sun nuna samun ayyukan bukatun jama'a na farko, ta fuskar tsaron abinci, kiwon lafiya, ilimi, yaki da jahilci da samar da ayyukan yi. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku