in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faure ya lashe zaben shugabancin kasar Togo a karo na uku
2015-04-29 10:32:53 cri
Hukumar zaben kasar Togo ta sanar a daren ranar talata Talata cewa, shugaban kasar na yanzu Faure Essozimna Gnassingbé ne ya lashe zaben da aka gudanar a ranar asabar 25 ga wata, abinda ya bashi damar sake ci gaba da zama shugaban kasarhakan ya zama karo na uku da ya lashe zaben shugabancin kasar.

Bisa sakamakon da hukumar zaben kasar Togo ta bayar, Foure ya samu kuri'u da kashi 58.75 cikin dari, yayin da dan takara na jam'iyyar kawancen neman yin kwaskwarima kan siyasa ta kasar Jean Pierre Fabre ya samu kuri'u da kashi 34.95 cikin dari, haka kuma adadin kuri'un da sauran 'yan takara uku suka samu bai zarce kashi 7 cikin dari ba.

Bisa dokar zaben kasar Togo, idan anana gudanar dajefa kuri'u karo daya kawai zagaye farko a zaben shugabancin kasar, kuma wanda ya fi samun kuri'u ne zai zama shugaban kasar. Ana bukatar daYanzu ana jiran kwamitin tsarin mulkin kasar da ya tabbatar da sakamakon da hukumar zaben kasar ta bayar.

Foure mai shekaru 48 da haihuwa, ya fara zama shugaban kasar Togo ne a karon farko a watan Afrilu na shekarar 2005, sannan ya samu zarcewayi nasarar sake hawan kujerar a karo na biyu a shekarar 2010. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China