in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala aikin canja hukumomin rundunar sojoji a kasar Sin
2016-02-02 09:59:44 cri
Darektan hukumar kula da yada labaru na ma'aikatar tsaron kasar Sin kuma kakakin ma'aikatar Yang Yujun ya furta a jiya Litinin 1 ga wata cewa, bayan da aka sake canja tsarin rundunar sojojin kasar, an kafa hukumomin ba da umurni cikin hadin gwiwa a wasu yankunan kasar, abun da ya samar da babban ci gaba cikin tarihin sojojin 'yantar da jama'ar kasar Sin, wanda kuma zai ba da tabbaci ga sojojin su kware wajen yaki da gudanar da aikin tsaron kai, kuma batun yana da ma'anar musamman sosai.

A ranar litinin 1 ga wata, ma'aikatar tsaron kasar Sin ya shirya taron manema labaru, inda Mr. Yang Yujun ya ce, a wannan karo, an canja tsoffin hukumomin sojoji 7, kuma an kafa hukumomin yankunan yaki guda 5, kuma kwamitin tsakiya na soji na kasar Sin ya shugabanci wannan aiki. An kafa hukumomin yankunan yaki don ba da umurni wajen yake-yake cikin hadin gwiwa tsakanin rundunoni na yankuna daban daban, da gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya da tinkarar kalubalen da ake fuskanta, ta yadda za a cimma nasara duk lokacin da wani yaki ya barke.

Yang Yujun ya ce, yanzu, an kammala aikin kafa hukumomin yaki a yankunan daban daban na kasar.

Ya kara da cewa, a kullum kasar Sin tana bin manufar tsaron kai, kuma za ta tashi tsaye don gudanar da wannan manufa, ko ta kaka ba zata canja wannan manufa ba.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China