Zambiya: Tallafin kudi daga masu bada lamuni na duniya domin karfafa tattalin arzikinta
2016-01-28 10:58:37
cri
Kasar Zambiya zata samu wani tallafin kudi mai tsoka daga kasashe masu bada lamuni bisa kudurin da aka tsayar yayin babban taron ministoci na kungiyar kasuwanci ta duniya (OMC) karo na goma da ya gudana a kasar Kenya a cikin watan Disamban da ya gudana. Zambiya zata amfana da shirin Enhanced Integrated Framework (EIF), tsarin dake aiki da masu bada lamuni da dama bisa manufar taimakawa kasashen maras samun cigaba wajen taka rawa sosai a cikin tsarin kasuwancin duniya tare da ba su damar yin amfani da kasuwanci a matsayin wani ginshikin cigaban tattalin arziki da rage talauci. (Maman Ada)