in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Faransa ta jibge sojoji don tabbatar da tsaron a yayin taron sauyin yanayi na Paris
2015-11-26 10:03:43 cri
Ministan kula da harkokin cikin gida na kasar Faransa Bernard Cazeneuve, ya ce sakamakon mummunan harin ta'addanci da aka kai a birnin Paris a ranar 13 ga watan nan, Faransa za ta jibge 'yan sanda da sojoji dubu 11, don ba da tabbaci ga tsaron babban taro da za a gudanar dangane da sauyin yanayi a karshen wannan wata.

A gun taron manema labaru da ma'aikatar kula da harkokin cikin gidan kasar ta shirya, ministan ya bayyana cewa 'yan sanda kimanin 8000 ne za su gudanar da bincike a kan iyakokin kasar ta Faransa. A sa'i daya kuma, za a kara tura ma'aikata kimanin 2800 don tabbatar da tsaron a wurin taron.

Har wa yau a daya bangaren, rundunar sojin birnin na Paris ta ce domin saukakawa shugabannin kasashen duniya zirga-zirga, da isa wurin da za a gudanar da taron, za a dauki matakan hana zirga-zirgar motoci a wasu hanyoyi da ke kewayen birnin Paris, da ma wasu manyan hanyoyi, baya ga hanyoyin da ke kewayen manyan filayen jiragen sama na Charles de Gaulle, da na Orly dake birnin.

Fadar shugaban kasar Faransa ta bayyana cewa, an gayyaci shugabanni da kusoshin gwamnatocin kasashe 138 don halartar taron.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China