in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jaddada muhimmancin raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba
2016-01-07 20:35:01 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya kira wani taron bita a yayin rangadin aikin da ya kai birnin Chongqing a kwanan baya, inda ya saurari shawarwari da ra'ayoyi dangane da yadda za a kara kokarin bunkasa yankin tattalin arziki na kogin Yangtze.

A yayin taron, shugaba Xi ya jaddada cewa, kogin Yangtze, shi ne mahaifar al'ummar Sinawa, haka kuma babban ginshiki ne wajen raya al'ummar Sinawa. Don haka dole ne a yi la'akari da irin moriyar da al'ummar za su dade suna girba yayin da ake kokarin bunkasa yankin tattalin arziki na kogin. Bugu da kari, wajibi ne a mayar da hankali wajen kiyaye muhalli yayin da ake kokarin raya yankin, a kokarin cin gajiyar kyakkyawan muhalli tare da samun riba da alheri ga jama'a, ta yadda kogin na Yangtze zai yi ta bunkasa har abada. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China