Cikin sanarwar, kwamitin ya nuna juyayi ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su, ya kuma nuna fatan wadanda suka jikkata za su iya samun sauki cikin sauri, kana ya mika sakon ta'aziya ga gwamnati da jama'ar kasa ta Indonesia.
Bugu da kari, kwamitin sulhu na MDD ya jaddada cewa, ya kamata a gurfanar da wadanda suka shirya da kuma aikata laifuffukan ta'addanci gaban kuliya da sauri, haka kuma da wadanda suka samar da kudi da kuma nuna goyon baya ga harkokin ta'addanci. (Maryam)