in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 7 sun mutu sakamakon fashewar bom a birnin Jakarta na Indonesia
2016-01-14 21:15:28 cri

'Yan sandan kasar Indonesia sun bayyana a yau Alhamis cewa, yawan mutanen da suka rasu, a sakamakon harin bam da aka kai cibiyar sayar da kayayyaki dake tsakiyar birnin Jakarta hedkwatar kasar sun kai mutum 7, yayin da kuma wasu 17 suka ji rauni.

Mai magana da yawun rundunar 'yan sandan kasar Mista Ikbal, ya ce wadanda suka aikata wannan ta'asa su biyu suma sun rasu, yayin da suka tada bam din da ke jikinsu, kana 'yan sanda sun harbe ragowar maharan uku.

Mista Ikbal ya kara da cewa, ya zuwa yanzu, an cafke wasu dake da hannu a kaddamar da harin, baya ga harbe sauran daga cikin su, matakin da ya dawo da kwanciyar hankali a kasar.

A nasa bangare, kakakin babbar hukumar 'yan sandan kasar Mista Anton Charliyan, ya musanta aukuwar tashin boma-bomai masu yawa, inda ya ce an kai harin ne kawai kan cibiyar sayar da kayayyaki ta Sarinah, da tashar 'yan sanda masu lura da ababen hawa dake daf da ita.

Dadin dadawa, shugaban kasar Mista Joko Widodo, ya fidda wata sanarwa a wannan rana, yana mai bayyana harin da aka kai a matsayin aikin ta'addanci, sa'an nan ya yi kira ga bangarori daban-daban, da su kaucewa yada jita-jita, gabanin fitar da cikakken sakamakon binciken da ake gudanarwa a yanzu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China