in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin ruwan ceto na Sin ya tashi zuwa yankin teku inda ake laluben ragowar jirgin saman Air Asia
2015-01-07 20:35:01 cri
A Larabar nan kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, ya bayyanawa wani taron manema labaru cewa, gwamnatin Sin, da rundunar sojin kasar a shirye suke su kara yawan ma'aikatan da ke gudanar da aikin laluben ragowar jirgin saman nan na AirAsia da ake ci gaba da gudanarwa bisa bukatar kasar Indonesia,

Hong Lei ya ce, bisa bukatar kasar ta Indonesia, rukunin masana na hukumar lura da jiragen saman fasinja ta kasar Sin, tuni ya isa yankin tekun kasar, tare da na'urorin zamani, domin neman akwatin nadar bayanan jirgin, yayin da jirgin ruwan ceto mai lamba 101, dake yankin tekun Kudu na ma'aikatar sufurin Sin ya gaggauta tashi zuwa yankin tekun, dauke da na'urar laluben akwatin nadar bayanai, da na tarkacen jiragen saman.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China