Gabon: An kaddamar da ayyukan zabuka bisa shirin zaben shugaban kasa na shekarar 2016
anar Talata a birnin Libreville da ayyukan zabuka bisa shirin gudanar da zaben shugaban kasa na shekarar 2016 da kuma na 'yan majalisu da aka tsaida a karshen shekarar. An gudanar da bikin ta hanyar bude wani taron karawa juna ilimi ga wasu 'yan kasar Gabon gomai da aka rike su a cikin wasu jerin tawagogin diplomasiyya dake kasashen waje na kasar domin 'yin rijstan dukkan 'yan kasar Gabon dake ketare kan rijistan zabe.
Horon ya gudana a karkashin jagorancin sakatare janar na ma'aikatar, Lambert Noel Mata. Kundin tsarin mulkin kasar Gabon dai ya baiwa 'yan Gabon dake waje damar halarta zaben shugaban kasa. Sai dai kuma ba za su halarci zaben 'yan majalisu da na kananan hukumomin ba. (Maman Ada)