in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardar MDD ya damu game da karuwar harin sama da ake yi a Yemen
2016-01-09 13:24:57 cri
Magatakardar MDD Ban Ki-Moon a ranar Jumma'an nan ya bayyana damuwa game da karuwan hari ta sama da kasashen kawance ke yi da kuma fada a kasa har ma da jefa bama bamai a Yemen duk da kiraye kiraye na bukatar tsakaita bude wuta, in ji kakakin majalissar Stephane Dujjaric.

A ganawar da ya yi da manema labarai a wannan rana, ya ce Mr Ban musamman ya fi damuwa game da rahotannin dake nuna karuwan harin sama a wuraren da akwai mazauna da kuma gidajen jama'a a sana'a da suka hada da ofishin ciniki, zaurukan bikin aure da cibiyar makafi.

Mr. Ban ya tunatar da dukkan bangarorin a kan muhimmancin dake akwai na mutunta nauyin da ya rataya a wuyansu karkashin dokar kare hakkin bil adama wanda ya haramta kai hari kai tsaye a kan fararen hula ko muhallan su, in ji Dujjaric.

Magatakardar na MDD daga nan kuma ya yi kira ga dukkan bangarorin dake fada da juna a Yemen da su yi huldar cikin aminci da wakilin shi kuma manzon musamman a Yemen domin samar da daman aiwatar da wani zagayen tattaunawar ta ba da dadewa ba. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China