in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bangarorin da rikicin Yemen ya shafa sun zargi da juna da sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wuta
2015-12-17 10:02:41 cri
Yayin da wakilan bangarori daban daban da rikicin Yemen ya shafa suke yin shawarwarin shimfida zaman lafiya a kasar Switzerland, dakarun kungiyoyin kasar kuma sun zargi da juna da sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta wucin gadi da MDD ta bukaci a sanya hannu a ranar 16 ga wata.

Gwamnatin kasar Yemen ta zargi dakarun Houthi da rashin girmama yarjejeniyar, inda suka ci gaba da gudanar da aikin soja. Bayan wasu mintuna da sanar da yarjejeniyar tsagaita bude wutar a ranar Talata, dakarun Houthi sun kai hari a yankuna da dama na jihar Taiz da ke kudancin kasar.

Bugu da kari, dakarun sun kai hari a jihar Marib dake arewacin kasar, inda suka yi yunkurin sake kwace yankin da suka taba mamayewa a baya.

Ko da yake dakarun Houthi sun musunta wannan zargi, suna masu cewa, sojojin hadin gwiwa na kasa da kasa da kasar Saudiyya ke jagoranta sun sha saba yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka cimma, ganin yadda suka ta kai hare-hare ta sama a jihohi da dama, wadanda suka haddasa mutuwar mutane da dama. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China