in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da shirin fara tattaunawa kan zaman lafiyar Yemen da za'a fara a Switzerland
2015-12-16 09:47:35 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon, a ranar Talatar nan ya goyi bayan shirin kaddamar da tattaunawa kan batun zaman lafiyar kasar Yemen wanda za'a gudanar a kasar Switzerland, da ake saran farawa daga yau Laraba, a matsayin wani bangare na warware rikicin sojin wanda ya dabaibaye kasar.

A wata sanarwa dauke da sa hannun mista Ban, mai Magana da yawun babban sakataren ta ce, Ban ya yi amanna cewar, ta hanyar tattaunawa ne kadai za'a warware rikicin kasar, da kuma tabbatar da samun fahimtar juna a tsakanin alummomin kasar ta Yemen, bayan fuskantar yakin basasa na tsawon watanni wanda ya yi sanadiyyar lakume rayukan dubban jama'a a kasar.

Kazalika Ban, ya yi maraba da matakin da bangarorin da ba sa ga maciji da juna a kasar suka dauka, na yin alkawarin tsakaita wuta a yayin da ake shirin kaddamar da tattaunawar.

Sannan ya bukaci dukkannin bangarorin kasar da su mutunta wannan yarjejejniyar, domin gudanar da ayyukan da za su tabbatar da samun dawwamamman zaman lafiya a kasar.

Bugu da kari, babban sakataren, ya bayyana kyakkyawar fatarsa na cewar tattaunawar zata kawo karshen rikicin sojin a Yemen, kuma zata sanya kasar kan turbar zaman lafiya mai dorewa.

Sannan ya yi kira ga bangarorin kasar da su kai zuciya nesa , kuma su amince wajen aiwatar da matakan da zasu kawo karshen mawuyacin halin da al'ummar kasar ke ciki, domin jama'a su samu damar gudanar da al'amuran su na yau da kullum.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China