in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi maraba da aniyar bangarorin kasar Yemen ta hawa teburin sulhu
2015-12-24 10:35:51 cri
Kwamitin sulhun MDD ya fidda wata sanarwa a jiya Laraba, wadda ke kira ga bangarori daban daban da rikicin kasar Yemen ya shafa, da su dakatar da kaiwa juna hari, kana kwamitin ya yi maraba da aniyar bangarorin na alkawarin sake komawa teburin shawara da nufin cimma nasarar shimfida yanayin zaman lafiya, matakin da ake fatan dauka cikin watan Janairun shekara mai zuwa.

Sanarwar ta bayyana cewa, kwamitin sulhun ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar Yemen, da su komawa shawarwari ba tare da gindaya wani sharadi ba, su kuma warware matsalolinsu ta hanyar gudanar da shawarwari.

Kaza lika kwamitin tsaron ya bukace su da su kaucewa tsokanar juna, da sauran matakan da ka iya haifar da illa ga yanayin wucin gadi a fannin siyasar kasar. Mambobin kwamitin sulhun sun kuma yi tir da dukkanin wasu matakai na nuna karfin tuwo ga masu gudanar da shawarwarin.

Bisa shirin shiga-tsakani na MDD, bangarori daban daban da rikicin kasar Yemen ya shafa, sun fara gudanar da shawarwarin shimfida zaman lafiya tun daga ranar 15 ga watan nan, inda suka cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta kwanaki 7, wadda aka fara aiwatar da ita nan take.

Sai dai bayan kwana guda da daukar wannan mataki, sojojin gwamnatin kasar Yemen da dakarun Houthi, sun zargi da juna da sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wutar, inda suka ci gaba da kaiwa juna hari.

Game da hakan, manzon musamman na MDD mai kula da batun Yemen Ismail Ould Cheikh Ahmed, ya sanar a ranar 20 ga wata cewa, za a sake komawa teburin shawarwari a tsakiyar watan Janairun shekarar dake tafe. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China