in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya sa lura ga bala'in gangarowar duwatsu a Shenzhen
2015-12-21 13:24:27 cri
An samu aukuwar bala'in gangarowar duwatsu a wani yankin masana'antu dake birnin Shenzhen, a lardin Guangdong a ranar Lahadi 20 ga watan nan, da misalin karfe 11 da minti 40 bisa agogon wurin, inda wannan hadarin ya sa aka samu fashewar wasu abubuwa a bututun jigilar iskar gas dake wurin. Ya zuwa karfe 9 safiyar yau Litinin, kasar da ta yi gangarowa ta binne gidaje da gine-gine 22, kana mutane 3 sun ji rauni, yayin da wasu mutane 91 suka bace.

Bayan faruwar bala'in, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bada umurni ga hukumomin lardin Guangdong, da na birnin Shenzhen, da su gudanar da aikin ceto nan da nan, su kuma bada jinya ga mutanen da suka ji rauni, da jajantawa iyalan wadanda suka ji rauni ko suka bace. Ya ce ya kamata a gudanar da aikin ceto ta hanyar da ta dace, da magance sake faruwar bala'in.

Hukumomin kwamitin tsakiya na jam'iyyar Kwaminis ta Sin, sun jagoranci hukumomin larduna da birane, wajen kara bincike a fannin magance bala'i da hadari, da tsara shirye-shirye, da tsarin bayar da gargadin kare kai, da aikin tsugunar da mutanen da bala'u suka shafa, don tabbatar da tsaron jama'a da na dukiyoyinsu.

A halin yanzu, ana gudanar da aikin ceto yadda ya kamata a yankin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China