Hukumar hadin gwiwa ta bada umurni ta sojojin kasar Iraki ta bayar da sanarwa a wannan rana cewa, jiragen saman yaki na sojojin kasar Iraki sun kai hari ga wani gini na birnin al-Qaim da ke iyakar Iraki da Syria da ke hannun dakarun kungiyar IS, harin da ya haddasa mutuwar wasu dakarun kungiyar IS dake cikin ginin, ciki har da madugan kungiyar 5 wadanda suka tsara shirin kai hari ga manyan hafsoshi 2 na sojojin kasar Iraki a ranar 27 ga wata. Amma sanarwar ba ta bayyana hakikanin lokacin da aka kai harin ba.
Sanarwar ta bayyana cewa, bayan da hafsoshin biyu suka mutu a sakamakon harin, hukumar leken asiri da hukumar hadin gwiwa ta bada umurni ta sojojin kasar sun kaddamar da bincike don zakulo dakarun kungiyar IS da suka tsara shirin kai harin. A karshe an gano cewa sun buya ne a wani wuri a birnin al-Qaim dake da nisan kilomita kimanin 330 arewa maso yammacin birnin Baghdad . (Zainab)