in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An hallaka Zahran Alloush, jagoran dakarun Islam a Sham
2015-12-26 13:49:57 cri
A jiya Jumma'a 25 ga wata, hedkwatar rundunar sojan gwamnatin kasar Sham ta fitar da wata sanarwa, inda ta amince da cewa, an hallaka Zahran Alloush, jagoran dakarun Islam masu adawa da gwamnatin yanzu, a cikin wani harin sama da sojojin sama na gwamnatin kasar suka kai a ranar kan wani sansanin rundunar dakarun Islam dake karkarar birnin Damascus.

Wannan sanarwa ta kara da cewa, bayan da dakarun gwamnatin kasar Sham suka dauki jerin matakan sa ido, bisa amintaccen bayanin da aka samu, an ce, dakarun sojan gwamnatin sun kai hari daga sama kan sansanin rundunar dakarun Islam, inda ba ma kawai aka hallaka Zahran Alloush ba, har ma da wassu jagora na dakaru masu dauke da makamai na Rachman da na Ahrar al-Sham wadanda suke nuna adawa da gwamnatin kasar ta yanzu.

Wannan sanarwa ta kuma jaddada cewa, dakarun gwamnatin Sham za su ci gaba da dakile kungiyoyi masu tsatsauran ra'ayi har sai an rushe su gaba daya. A waje daya kuma, wannan sanarwa ta yi kira ga dukkan masu dauke da makamai da su ajiye makamansu, su koma al'ummominsu na halal, sannan ana fatan su bayar da gudummawarsu wajen tsaron kasar, da kawar da ta'addanci daga kasar. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China