in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar hadin gwiwa ta binciken makamai masu dauke da sinadarai na Syria ya fara aiki
2015-11-14 16:19:34 cri
Hukumar bincike ta hadin gwiwwa kan makamai masu dauke da sinadarai na kasar Syria ya fara aiki sosai ta inda ya dauki ma'aikatan sashin gudanarwa sakamakon taron shi na farko, in ji kakakin MDD Farhan Haq a ranar Jumma'an nan.

A cikin watan jiya, hukumar ta kuma yi yunkurin kafa ofishin shi a cibiyar MDD dake birnin New York da kuma Haque na kasar Netherlands, sannan kuma da wani a birnin Damascus na kasar Syria, in ji Mr. Haq a lokacin ganawar da ya yi da manema labarai a wannan rana.

Ya yi bayanin cewa hukumar ta hadin gwiwwa a yanzu yana da isassun ma'aikata da zai iya cewa ya fara aiki yadda ya kamata da wannan rana.

Babban sakataren kwamitin tsaron Majalissar ya aike da wasika dangane da hakan a ranar 10 ga wannan watan na Nuwamba. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China