in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyoyin 'yan adawar Syria na taro a Riyadh
2015-12-09 20:20:42 cri
Kungiyoyin 'yan adawar gwamnatin kasar Syria daga ciki da wajen kasar suna wani taro a birnin Riyadh na kasar Saudiya da nufin kawo karshen rikicin kasar.

Gabanin bude taron na Saudiya, manyan 'yan adawar kasar sun bayyana aniyarsu ta halartar taron sasantawan, wanda ake fatan zai samu halartar jami'an diflomasiya na kasashen ketare ciki har da na kasar Rasha.

Kungiyar kawance ta Syria wato SNC a takaice, ta ce za ta yi amfani da wannan dama wajen hada kan dakarun 'yan adawa a kokarin da ake na kafa gwamnatin hadaka bisa tsarin yarjejeniyar da aka cimma tun farko a birnin Geneva.

Rahotanni na cewa, sama da wakilai 100 ke halartar taron da ministan harkokin wajen kasar ta Saudiya ya bude. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China