Pete Manfield, Shugaban ofishin a lokacin ganawa da manema labarai a Nairobin Kenya ya ce ana bukatar Karin kayayyaki domin taimaka ma al'umma a wannan shiyya su jure sakamaon fitinar ya nayin na el nino da zasu fuskanta.
El-Nino yana kara ruruta yanayin jin kai da ake fuskanta a shiyyar. A yanzu haka an yi kiyasin mutane miliyan 2 za su iya rasa muhallan su idan ruwan sama mai karfin gaske na wannan el ninon ya taho don haka ake bukatar gaggauta samun kudin kai dauki.
Ofishin na MDD a makon jiya yayi gargadin cewa ruwan sama mai karfin gaske na El-Nino zai kara munanta yanayin karancin abinci da barkewar cututtuka a wannan shiyya na kusurwar Afrika.(Bello Wang)