in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da shawarar majalissar dokokin bangaren adawa na Libya kan amincewa da sa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya
2015-12-12 13:02:23 cri
Kwamitin tsaro na MDD a ranar Jumma'an nan ta yi maraba da shawarar da bangarori biyu dake adawa da juna na majalissar dokokin kasar Libya suka yi ta saka hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiya a ranar 16 ga wata.

Samantha Power, wakiliyar kasar Amurka wadda take rike da shugabancin kwamitin na wannan watan ta sanar da hakan lokacin da take zantawa da manema labarai bayan wani tattaunawar sirri da kwamitin ta yi game da Libya.

A safiyar wannan rana, wakilin bangaren adawa na GNC masu ra'ayin addinin Islama a kasar Saleh al-Makhzun shi ma ya tabbatar da wa'adin karshen na rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiyar. Yana mai bayanin cewa tattaunawar da kwamitin sulhun MDD ta kira shi ne ya fi dacewa. Ya ce wannan yarjejeniyar za ta samar da makoma mai amince ga al'ummar kasar ta Libya.

Libya dai ta fada cikin rikicin siyasa tun bayan da aka samu majalissan dokoki da gwamnatoci guda biyu masu adawa da juna da kowannen su ke ikirarin jan ragamar mulkin kasar bayan halin rashin tsaro da aka shiga tun kifar da gwamnatin marigayi Mu'ammar Ghaddafi. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China