in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 5 sun hallaka a kudu maso gabashin jamhuriyar Nijar sanadiyyar harin Boko Haram
2015-12-24 09:33:56 cri
Wata majiya daga jami'an tsaro na yankin Diffa na kasar Nijar ta ce, a kalla mutane biyar ne suka gamu da ajalinsu, kuma biyu daga cikin su sojoji ne, sannan wasu mutanen da dama suka jikkata a yayin wani harin ta'addanci na mayakan Boko Haram da safiyar ranar Laraba a kauyen Abadam, wanda ke shiyyar kudu maso gabashin Jamhuriyar Nijer.

Sauran mutane ukun da suka mutu, 'yan asalin kauyen Abadam ne, kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua, ya tuntubi majiyar domin sanin adadin wadanda suka mutu daga bangaren maharan, sai dai ba'a bayyana adadin ba, amma an ce maharani sun tsere zuwa wasu sassa na Najeriya wacce ke makwabtaka da Nijar.

Wadannan hare haren na sari ka noke daga Boko Haram a yanki Diffa, suna zuwa ne bayan da hukumomin jamhuriyar Nijar suka ayyana kafa dokar ta baci a yankin Diffa watanni da dama da suka gabata.

Tun a watan Fabrairun wannan shekara, yankunan Bosso da Diffa, wadanda ke makwabtaka da Najeriya ke fama da hare haren Boko Haram babu kakkautawa, lamarin da yayi sanadiyyar rayukan daruruwan fararen hula da kuma jami'an sojoji. Haka zalika, a daidai wannan lokacin, sama da mayakan Boko Haram 1,000 ne sojojin Najar suka hallaka.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China