in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin CGC na kasar Sin ta daf da kammala ginin asibitin kwararru a janhuriyar Nijar
2015-09-10 19:16:33 cri
Nan gaba kadan ne ake fatan bude wani katafaran asibitin kwararru a birnin Yamai na janhuriyar Nijar, aikin da kamfanin CGC na kasar Sin ke gudanarwa a yanzu haka. Wanda kuma zai lashe kudi har dalar Amurka miliyan 66, kudin da kasar Sin ta ba da shi a matsayin tallafi.

Da yake jawabi yayin ziyarar da ya kai wurin da ake gudanar da aikin ginin, shugaban kasar ta Nijar Mahamadou Issoufou ya nuna gamsuwa da yadda aikin ke gudana, wanda ya zuwa yanzu ya kai kaso 85 cikin dari.

Rahotanni sun bayyana cewa bayan kammalar aikin, asibitin zai samar da gadajen kwanciya sama da 500, zai kuma baiwa marasa lafiya damar samun jiyya a fannoni daban daban, kama daga masu bukatar jiyyar gaggawa, ya zuwa cututtukan da suka shafi zuciya, da kuma dakunan tiyata 12, baya ga dakunan bincike da sauran su. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China