in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijar da Chadi sun dauki niyyar sanya layukan raba iyaka tsakaninsu
2015-11-12 10:04:26 cri
Hukumomin kasashen Nijar da Chadi sun amince da gudanar nan ba da jimawa ba da aikin sanya layin raba iyaka tsakaninsu da kasashen biyu suka gada daga uwar mulkinsu ta kasar Faransa a shekarar 1960, mai tsawon daruruwan kilomita, a cewar wata majiya a birnin Niamey.

Gwamnatin Nijar ta shigar a ranar Talata a yayin wani taron ministoci da dokar dake bada damar rattaba hannu kan yarjejeniyar da ta shafi kafa wani kwamitin hadin gwiwa dake hurumin aiwatar da wannan layin iyaka, da aka sanya ma hannu a ranar 5 ga watan Yulin shekarar 2013 a birnin Niamey.

Kwamitin an dora masa nauyin tattara bayyanai da yin nazari kan takardun da ake tsammanin zasu kawo karin haske game da shata layin iyaka tsakanin kasashen biyu, da kuma tattara bayanai da binciken matsalolin dake da nasaba da shari'a, siyasa, tattalin arziki da jama'a, da aiwatar da wannan layin raba iyaka zasu janyo da gabatar da mafita ta yadda za'a daidaita batun, da kuma fara aikin sanya layin raba iyaka.

Bangarorin biyu sun dauki niyyar baiwa kwamitin hadin gwiwa duk wasu takardun da zasu kawo karin haske kan layin raba iyaka tsakanin kasashen biyu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China