in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta harba tauraron dan Adam na kasuwanci karo 42
2015-12-23 13:33:07 cri

An yi taron dandalin tattaunawa na bunkasuwar zirga-zirgar sararin samaniya na kasa da kasa karo na 3 a jiya Talata a nan birnin Beijing, inda aka bada labarin cewa, ya zuwa watan Disambar wannan shekara ta 2015, kasar Sin ta kammala harbar tauraron dan Adam na kasuwanci karo 42, inda yawan tauraron dan Adam da ta harba ya kai 48.

A sakamakon bunkasuwar harkokin zirga-zirgar samarin samaniya ta kasar Sin, an samu sakamako mai kyau wajen yin hadin gwiwa tare da sauran kasashen duniya a wannan fanni. Ya zuwa watan Disamba na wannan shekara, kasar Sin ta kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa tare da kasashen Rasha, da Brazil, da Pakistan, da Venezuela da kuma sauran kasashe da hukumomi fiye da 30, don raya harkokin zirga-zirgar sararin samaniya. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China