in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya sake tsawaita iznin samar da gudummawa ga Syria
2015-12-23 11:13:53 cri
Kwamitin sulhun MDD ya zartas da wani kuduri a jiya Talata, na tsawaita iznin samar da gudummawa ga jama'ar kasar Syria da shekara guda, domin hukumomin jin kai na MDD, da bangarorin gudanarwar kudurin su samu damar isar da tallafi kamar yadda ya kamata. Bisa wannan sabon kudiri, za a ci gaba da samar da taimako ga al'ummar kasar ta Syria har ya zuwa ranar 10 ga watan Janairun shekarar 2017.

Kaza lika, a karkashin wannan kuduri, mahukuntan kasar Syria, da hukumomin jin kai na MDD suna da ikon ratsa wurare hudu na kan iyakar kasar ta Syria da kasashen Turkiya, da Iraki, da Jordan, bayan sun sanar da mahukuntan kasar Syria. Domin samar da kayayyakin jin kai zuwa wurare daban daban na kasar Syria.

Mataimakin wakilin Sin dake MDD Wang Min, ya gabatar da jawabi bayan zartas da kudurin, ya na mai cewa Sin ta yi maraba da kwamitin don gane da zartas da kudurin mai lamba 2258. Ya ce Sin na goyon bayan hukumomin jin kai na MDD, wajen gudanar da ayyukan jin kai bisa tushen girmama ikon mulkin kasar Syria, domin daidaita kasa da kasa da su ba da gudummawa. Sin ta yi kira ga bangarori daban daban da wannan batu ya shafa, da su sauke nauyin dake kan su na aiwatar da sabon kuduri, da ma sauran kudurorin dake da alaka da shi, tare da tabbatar da samar da gudummawar jin kai, da sassauta mawuyacin halin da jama'ar kasar Syria ke ciki.

Wang Min ya kara da cewa, hanyar siyasa ita ce hanya daya kacal ta warware batun kasar Syria, kana ita ce tushen kyautata halin jin kai na al'ummar kasar, da ma magance matsalar 'yan gudun hijirar Syrian. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China