in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta jaddada muhimmancin dakatar da bude wuta a Syria domin yaki da ta'addanci
2015-11-15 14:20:22 cri
Kasar Sin ta jaddada muhimmacin tsagaita bude wuta baki daya a Syria domin yaki da ta'addanci.

Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Li Baodong, dake bayani a gaban manema labarai a ranar Asabar a birnin Vienna, inda yake halartat wani taron kasa da kasa kan rikicin Syria, ya bayyana cewa akwai bukatar a cimma tsagaita bude wuta baki daya a Syria, idan ana fatan gamayyar kasa da kasa ta yaki kowa ne irin ta'addanci cikin hadin gwiwa.

Taron kan ricikin Syria na gudana kwana daya bayan hare haren ta'addancin da suka abku a birnin Paris, wadanda suka yi sanadiyyar mutuwar mutane kimanin 129 da raunana 352.

Mataimakin ministan harkokin wajen Sin ya kuma bayyana ra'ayin cewa gyare gyaren da za'a yi domin wani rikon kwarya a Syria dole su yi dogaro kan sanarwar Geneva da kuma kasancewa a karkashin jagorancin MDD.

Mista Li Baodong yayi kira da a kara karfafa kokarin bada agajin kasa da kasa, tare da yin alkawarin cewa kasar Sin zata dauki matakai a wannan fanni. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China