in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya halarci taron ministoci kan batun Syria na kwamitin sulhun MDD
2015-12-19 15:57:02 cri
A jiya Jumma'a 18 ga wata, ministan harkokin waje na Sin Wang Yi ya halarci taron ministoci kan batun Syria na kwamitin sulhun MDD a birnin New York.

A wajen taron, kwamitin sulhu ya zartas da kuduri mai lamba 2254 na amincewa da sakamakon da aka samu a gun taron ministocin harkokin waje na kungiyar goyon bayan Syria ta duniya, kasar Sin ita ma ta jefa kuri'ar amincewa.

Bayan zartas da kudurin, Wang Yi a jawabinsa cewa ya yi, wannan kuduri ya tattara ra'ayoyin kasa da kasa, kuma ya bayyana muhimmiyar rawa da kwamitin sulhun MDD ya taka, tare da zuba sabon karfi na daidaita batun Syria ta hanyar siyasa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China