in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta gabatar da shawarwar game da warwaren rikicin siyasar kasar Syria
2015-12-18 18:32:05 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana cewa, ministan harkokin wajen kasar Wang Yi zai gabatar da shawarwar a kan warware rikicin siyasar kasar Syria da yaki da ta'addanci a ranar Jumma'an nan a birnin New York.

Kakakin ya bayyana haka ne a yayin taron manema labarai da aka saba yi duk rana, ya kuma kara da cewa, Mr. Wang zai gabatar da shawarwarin da Sin take da su akan dakatar da bude wuta, cimma sulhu na siyasa, yaki da ta'addanci da kuma ayyukan da za'a gudanar bayan yaki.

Da yake bayyana goyon baya ga taron, Mr Hong Lei ya ce kasar ta Sin na fatan taron zai ingiza wani sulhuntawa a Syriyan sakamakon irin wannan ganawa har sau biyu a baya.

Bayan taron karo na uku na kungiyar, kwamitin tsaron MDD za ta kira taro a matakan ministoci duk a wannan ranar.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China