in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga bangarori daban daban da ke rikici a Yemen da su gaggauta yin shawarwari tsakaninsu
2015-06-16 13:43:22 cri
Sakatare janar na MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga bangarorin da rikicin kasar Yemen ya shafa da su tsagaita bude wuta a lokacin watan Azumi da ke karatowa, kuma ya bukaci bangarorin daban daban da su gaggauta komawa teburin yin shawarwari a siyasance.

A safiyar ranar 15 ga wata, a birnin Geneva, Ban Ki-moon ya gana da wakilan gwamnatin Yemen da za su halarci shawarwari a Geneva, inda bangarorin suka yi tattaunawa mai gamsarwa. A gun taron manema labaru bayan taron, Ban Ki-moon ya ce, daga watan Mayu na bana zuwa wannan lokaci, rikicin kasar ta Yemen ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kimanin 2600, rabi daga cikinsu fararen hula ne, abin da ke nuna mawuyacin hali, da kasar ta Yemen ta shiga.

Ban Ki-moon ya ce, hakkin bangarorin da abun ya shafa na Yemen shi ne su kawo karshen yake-yaken, da fara yunkurin zaman lafiya da sulhuntawa, a sa'i daya kuma, su ma kasashen duniya na da hakkin ba da goyon baya ga wannan yunkurin.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China