in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya ta tura sojoji dubu 25 a kan iyakokinta da Tunisiya
2015-06-28 13:27:27 cri
Kasar Aljeriya ta tura sojoji dubu 25 a kan iyakokinta da kasar Tunisiya, bayan harin da aka kaiwa 'yan yawon bude ido a ranar Jumma'a a gabar ruwan Sousse, in ji wata majiyar tsaron kasar Aljeriya.

Bisa wannan shirin, dakarun kasar Aljeriya na kara rubanya ayyukansu na bincike da sanya ido kan tashohin binciken jama'a da motoci domin kawar da duk wani yunkurin kutsa kan 'yan ta'addan da suka fito ko suke son shiga kasar Tunisiya.

A ranar Jumma'a ce, wani mutum ya bude wuta kan masu yawon shakatawa dake bakin ruwa da kuma wuraren ninkaya na gidan otel din Riu Imperial Marhaba dake Port El Kantaoui, kusa da Sousse (mai nisan kilomita 140 daga kudancin birnin Tunis), a arewa maso gabashin kasar Tunisiya.

Alkaluman baya baya sun nuna cewa mutane 39 aka kashe yayin 39 suka jikkata, kuma yawancinsu 'yan kasashen waje ne, in ji wata majiyar ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Tunisiya a ranar Asabar.

Kasashen Aljeriya da Tunisiya sun rattaba kan yarjeniyoyin dangantaka a fannin yaki da ta'addanci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China