in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ayew na kasar Ghana ya shiga jerin sunayen 'yan takarar neman lambar yabo na fitattun 'yan wasan kwallon kafa na Afrika
2015-12-16 15:35:57 cri

Fitaccen dan wasan nan na kasar Ghana wato mataimakin mai horas da 'yan wasa Andre Dede Ayew ya shiga cikin jerin sunayen mutane 3 da zasu yi takarar neman lashe kyautar lambar yabo ta hukumar shirya wasannin kwallon kafa na Afrika CAF na shekarar 2015, a matsayin fitaccen dan wasan kwallon kafan Afrika na wannan shekarar.

A ranar Litinin din nan CAF ta fitar da sunayen mutane ukun da zasu shiga takarar, wadan da suka hada da Andre Ayew na Ghana/Swansea City, da Pierre-Emerick Aubameyang na kasar Gabon na kulub din Borussia Dortmund, sai kuma Yaya Toure dan kasar Cote d'Ivoire na kulub din Manchester City

An zabi wadan da suka yi nasarar shiga takarra ne bayan da wata tawagar kwararru na shugabannin kungiyoyin kwallon kafa na CAF suka kada kuri'a.

Fitattun 'yan wasan Afrika na wannan shekara da suke zaune a Afrikan sune Baghdad Boundjah (Algeria/Etoile du Sahel), da Mbwana Aly Samata (Tanzania/TP Mazembe) da kuma Robert Kidiaba (DR Congo/TP Mazembe).

Za'a bayyana wadan da suka samu nasarar ne a wajen taron Glo-CAF Awards Gala, wanda za'a gudanar a ranar 7 ga watan Janairun shekarar 2016 a Abuja helkwatar Najeriya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China