in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Alves na Barcelona ya ce Neymar ya fi Ronaldo Kwarewa
2015-12-16 15:32:48 cri
Dan bayan kungiyar Barcelona Dani Alves, ya shaidawa wata jaridar kasar Brazil cewa, Neymar ya dara Cristiano Ronaldo no Real Madrid kwarewa a fagen tamaula. Alves na ganin babu wani dan wasa da za su goga da Neymar in banda Lionel Messi.

A zantawar ta sa da jaridar O Globo, Alves ya ce Neymar dan wasa ne da ya fi Ronaldo wuyar rikewa ga 'yan baya. Kaza lika ya fi sauran 'yan wasa iya sarrafa kwallo, da sauri cikin kuma kwarewa.

A ganin Alves Ronaldo ya na da tasiri wajen cin kwallaye da yawa, da kuma sanya kwallo a zare da ka, amma ba shi da gwanintar rike kwallo da sarrafata tsakanin 'yan wasa kamar Neymar.

A halin da ake ciki dai Neymar zai yi takarar karbar lambar bajimta ta Ballon d'Or, shi da Ronaldo da kuma Messi, a yayin bikin mika lambar da za a yi cikin wata mai zuwa.

Koda yake Alves bai tabbatar da hasashen cewa Neymar zai lashe lambar ta wannan karo ba, duk da haka ya ce akwai yiwuwar dan wasan mai shekaru 23 da haihuwa zai cimma wannan nasara a nan gaba.

Ya ce idan har Neymar na da burin lashe wannan lamba ko shakka ba bu zai cimma wannan bukata, idan yana son zama dana wasa mafi cin kwallaye a Brazil zai iya cimma hakan, duba da irin sha'awar da yake nunawa ga sana'ar sa ta kwallon kafa.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China